Menu

ADG Care Foundation Zata Yaye Daliban Farko a Shirin ta na Horas da Matasa 650 a Najeriya

Admin 9 months ago

 

Gidauniyar ADG Care Foundation ta yaye matasa 650 a matsayin rukunin farko da suka kammala horo a shirin ta na ƙasa na koyon ƙwarewar fasahar sadarwa (ICT) da aka fara a

Bikin yaye daliban ya gudana cikin kyakkyawan yanayi, inda jami’an gwamnati, shugabanni daga sassa daban-daban.

Shugabar gidauniyar ya bayyana cewa manufar shirin ita ce ba matasa damar koyon sana’o’in zamani da fasahar da za su taimaka musu su dogara da kansu a fannin aikace-aikace na zamani.
Daya daga cikin wadanda suka amfana da shirin, Ibrahim Musa daga Kano, ya ce:

“Shirin ya koya min yadda ake gina shafukan yanar gizo da sarrafa bayanai. Wannan horo ya buɗe min sabbin damar rayuwa.”

Shirin horon ya kunshi darussa kan tsara manhajoji (programming), tsaron bayanai a intanet (cybersecurity), da tallan kayayyaki ta hanyar dijital (digital marketing).
Gidauniyar ADG Care Foundation ta sha alwashin ci gaba da wannan aiki domin tallafa wa matasa da rage zaman banza a cikin al’umma, musamman ta hanyar fasahar zamani da ilimin sana’a.