Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Dr. Ali Makoda, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan mutuwar ɗalibai biyu a makarantar Kwana Sakandare da ke Bichi.
Ɗaliban da suka rasu, Hamza Tofawa da Umar Dungurawa, ana zargin wasu abokan karatunsu ne suka kai musu hari da wani ƙarfe da ake kira “Gwale-Gwale”.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Daraktan Wayar da Kai na Ma’aikatar Ilimi, Balarabe Kiru, ya fitar, inda aka rabawa manema labarai ciki har da jaridar The PUNCH a ranar Laraba.
A cewar sanarwar, kwamishinan, ta bakin Babban Sakataren Ma’aikatar, Bashir Muhammad, ya tabbatar wa jama’a cewa gwamnatin jihar za ta gudanar da bincike mai adalci da gaskiya tare da tabbatar da cewa kowa ya samu hakkinsa.
“An bayar da rahoton cewa wannan mummunan aiki ya faru ne bayan wasu manyan ɗalibai sun yanke shawarar hukunta waɗanda suka rasu bisa zargin aikata wani laifi,” in ji shi.
Babban Sakataren, wanda ya kai ziyara makarantar, ya ja hankalin ɗalibai da su zama masu lura da kuma kaucewa ɗaukar doka a hannunsu.
“Ku guji ɗaukar doka a hannunku, ku tabbata duk wani abin da ya dame ku kun kai rahoto ga hukumomin makaranta don ɗaukar mataki da ya dace,” in ji shi.

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Ambassador Dr. Amina Umar Namadi: A First Lady Defined by Compassion, Service, and Humanity
Police Rescue Abducted Three-Day-Old Baby, Arrest Two Suspects in Nasarawa
Governor Yusuf Mourns Alhaji Nuhu Dantani
ADC Leaders Reject INEC Decision, Vow to Resist, Mobilise Support in Otukpo
Police Disburse ₦9.26m to Families of Fallen Officers in Kano