Daga Abdullahi Kano
Matasa daga dukkan shiyyoyin kano wato kano ta kudu,arewa ta tsakiya sun gamu a kan cewa dan majalisar tarraya mai wakiltar kana nan hukumomin Rano , Kibiya da Bunkure shi ne dan takarar Gwamnan da yafi cancanta a zaben gwamnan kano a kakar zabe mai zuwa.
Matasan wadanda suka zanta da hairdar Time Express Nigeria a lokuta daban daban sunce Alhaji Kabiru Alhassan Rurum zakakuri ne,jangwarzo mai kishin alummarsa wanda zai iya mikewa a ko’ina ya wakilci alummarsa.
Wani matashi daga kano ta arewa mai suna Danlami shehu ya bayyana Alhaji Kabiru Alhassan Rurum da cewar shine mafi gogewa a fannin gudanar da mulki, iya mu’ammala da jama’a da kuma karrama dan Adam.
“Yayi mun gani domin kuwa ya rike shugaban majalisar dokokin jihar kano har karo biyu, salon jagorancinsa har yanzu ba’ayi ya tasa ba, kalli iron sum in ayyukan da ya kawo mana wannan yankin Namu, gaskiya munyi dace da farin wakili”
Haka dai jaridar time express tayi jin ra’ayoyin matasan jihar kano.
Mai karatu ko kasan wanene Alhaji Kabiru Alhassan Rurum?
Haifaffen Garin Rurum ne da ke karamar Hukumar Rano wanda ya tashi da kishin neman na kansa, kuma jajirtacce a a dukkan abin da ya Sanya a gaba, masoyin Alumma ne domin kuwa kullum a colon hidimar Alumma yake.
A wani sako da ya fitar a farkon watan Azumin nan Alhaji Kabiru Alhasaan Rurum ya bukaci alumma su dage da addua don samu tsira a nan duniya da lahira
Alh Kabiru Alhassan Rurum ya Kuma yi Kira ga malamai Musamman wadanda ke gudanar da tafsirai a irin wannan lokaci da su kasance masu Sanya Manya Zabukan kasa na 2023 da ke tafe cikin Adduo’in su, yayin tafsiri da lokacin hudubar Juma’a da sauran ibadu da ake gudanarwa Dan ganin anyi Zabukan lafiya an gama lafiya.
Turakin na Rano ya yi fatan Yadda aka ga farkon watan lafiya Allah yasa a gama ibadar lafiya, ya Kuma Sanya muyi ibada karbabbiya da Sakamakon ta shi ne ‘yan tawar Allah madaukakin Sarki.


Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
2027: INEC registers 155,133 new voters in Bauchi
Ambassador Dr Amina Namadi Launches Book, Distributes Educational Materials in Jigawa
May Day Without Meaning: The Silence of Empty Pockets
Bichi Moves Motion as Kano APC Stakeholders Endorse Tinubu for 2027, Raise N50m for Nomination Form
Yusuf Orders Probe into Alleged N1.5bn Salary Deductions in Kanoi
Fred Itua named Group Politics Editor, The Sun Newspaper