Menu

Zaben Gawamna 2023: Rurum shi ne zabinmu, shi yafi cancanta – Matasa

Admin 4 years ago

Daga Abdullahi Kano

Matasa daga dukkan shiyyoyin kano wato kano ta kudu,arewa ta tsakiya sun gamu a kan cewa dan majalisar tarraya mai wakiltar kana nan hukumomin Rano ,  Kibiya da Bunkure shi ne dan takarar Gwamnan da yafi cancanta a zaben gwamnan kano a kakar zabe mai zuwa.
Matasan wadanda suka zanta da hairdar Time Express Nigeria a lokuta daban daban sunce Alhaji Kabiru Alhassan Rurum zakakuri ne,jangwarzo mai kishin alummarsa wanda zai iya mikewa a ko’ina ya wakilci alummarsa.
Wani matashi daga kano ta arewa mai suna Danlami shehu ya bayyana Alhaji Kabiru Alhassan Rurum da cewar shine mafi gogewa a fannin gudanar da mulki, iya mu’ammala da jama’a da kuma karrama dan Adam.
“Yayi mun gani domin kuwa ya rike shugaban majalisar dokokin jihar kano har karo biyu, salon jagorancinsa har yanzu ba’ayi ya tasa ba, kalli iron sum in ayyukan da ya kawo mana wannan yankin Namu, gaskiya munyi dace da farin wakili”
Haka dai jaridar time express tayi jin ra’ayoyin matasan jihar kano.
Mai karatu ko kasan wanene Alhaji Kabiru Alhassan Rurum?
Haifaffen Garin Rurum ne da ke karamar Hukumar Rano wanda ya tashi da kishin neman na kansa, kuma jajirtacce a a dukkan abin da ya Sanya a gaba, masoyin Alumma ne domin kuwa kullum a colon hidimar Alumma yake.
A wani sako da ya fitar a farkon watan Azumin nan Alhaji Kabiru Alhasaan Rurum ya bukaci alumma su dage da addua don samu tsira a nan duniya da lahira

Alh Kabiru Alhassan Rurum ya Kuma yi Kira ga malamai Musamman wadanda ke gudanar da tafsirai a irin wannan lokaci da su kasance masu Sanya Manya Zabukan kasa na 2023 da ke tafe cikin Adduo’in su, yayin tafsiri da lokacin hudubar Juma’a da sauran ibadu da ake gudanarwa Dan ganin anyi Zabukan lafiya an gama lafiya.

Turakin na Rano ya yi fatan Yadda aka ga farkon watan lafiya Allah yasa a gama ibadar lafiya, ya Kuma Sanya muyi ibada karbabbiya da Sakamakon ta shi ne ‘yan tawar Allah madaukakin Sarki.