A kokarin ta wajen inganta ayyukan ta daidai da tsarin manufofin da aka kafa ta, hukumar kula da iyakokin ruwan kasar ta shirya taron bitar karawa juna sani na yini uku ga manyan jami’an ta.
A sanarwar da mataimakin darakta a sashin hulda da jama’a na hukumar Mr Edward Osagie ya rabawa manema labarai a birnin Ikko, yace Shugaban hukumar, Dr Bashir Yusuf Jamoh yayi bayanin cewa ganawa da masu ruwa da tsaki na cikin gida wani ginshiki ne na tabbatar da nasarar aiwatar da manufar samar da tsaro a iyakokin ruwan kasar nan da kuma inganta zirga-zirgar jiragen ruwa.
Dr Bashir Jamoh yace a kokarin cimma burin manufofin hukumar, hadin gwiwa daga dukkanin masu ruwa da tsaki ya zama wajibi don jawo hankulan masu zuba hannayen jari a bangaren iyakokin ruwan kasar nan.
Yayi nuni da cewa hukumar NIMASA ta maida hankali ne wajen aiwatar da manufar gwamnatin tarayya wajen jawo hankulan masu zuba hannayen jari, da kuma inganta hazakar ma’aikatan ta don yin gogayya da takwarorin su a fadin duniya.
A maqalar da ya gabatar, Darakta Janar na kwamitin tattalin arziki na kasa, Mr Laoye Jaiyeolawho ya lura da cewa bangaren iyakokin ruwan kasar nan na da muhimmiyar gudunmawar da za ta iya badawa wajen bunkasa tattalin arzikin kasa.
Ya kuma bukaci hukumar gudanarwar NIMASA da suyi dukkanin mai yiwuwa wajen ciyar da bangaren gaba daidai da cigaba na zamani.
Yayi nuni da cewa bisa la’akari da yakin Ukraine da Rasha da kuma sauyin da aka samu a duniya sakamakon barkewar cutar kwaronabairos, yin amfani da kimiyyar zamani zai taimakawa Nijeriya wajen samar da jagoranci a bangaren iyakokin ruwa.
Sanarwar ta kara da cewa hukumar NIMASA karkashin jagorancin Dr Bashir Yusuf Jamoh tana cigaba da shirya bitoci ga bangarori daban-daban na hukumar don samun nasarar aiwatar da manufofin kafa hukumar.
Shi dai wannan taron na bitar da aka shiryawa manyan jami’an hukumar na bana an tsara shi ne don cimma manufofin hukumar na gajere, matsakaici da dogon zango na shekaru takwas masu zuwa don inganta ayyukan hukumar.

Murtala Sule Garo yafi kowa Cancantar Zama Mataimakin Gwamnan Kano.
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da rufe karɓar biyan kuɗin Hajji na shekarar 2026.
TARON KOYAR DA KIWON KAJI DA KIFI: KPA
Dalung yayi Alhinin halin da Nigeria ke Ciki .
Manoma sun Kira ga Gwamnati Tarayya tayi taka Tsan-Tsan
Gwamna Peter Mbah na Enugu ya koma jam’iyyar APC
Yusuf Disburses N50,000 Monthly Support to 6,680 Women Across Kano
NSCDC Kano Command Tests Surveillance Drone to Boost Security Operations
Police Raid Criminal Hideout, Arrest Suspects, Recover Firearm, Illicit Substances in Akwa Ibom
CP Bello Inspects Police Constables Screening Exercise in Gusau
Police Repel Bandit Attacks in Maru, Bukkuyum LGAs of Zamfara